Mu ne ke da alhakin kashe sojojin Najeriya 11 - ISIS

Mu ne ke da alhakin kashe sojojin Najeriya 11 - ISIS

Mafi munin kungiyar ta'adda a doron kasa wato kungiyar ISIS (Islamic States of Iraq and Syria),ta yi ikirarin cewa ita ce ke da alhakin kai hari kan sojojin Najeriya a makon da ya gabata wanda ya yi sanadiyar salwantar rayukan dakaru 11 kamar yadda jaridar Reuters ta wallafa.

Kamar yadda ta wassafa a kafar watsa labaran ta ta AMAQ, kungiyar ISIS ta yi ikirarin cewa mayakan ta ke da alhakin kai mummunan hari a garin Gajiganni da ke jihar Borno a ranar Juma'ar da ta gabata.

Mu ne ke da alhakin kashe sojojin Najeriya 11 - ISIS
Mu ne ke da alhakin kashe sojojin Najeriya 11 - ISIS
Asali: UGC

Kafar sadarwa ta AMAQ a ranar Asabar ta watsa wasu hotuna dake haskaka irin munin ta'addanci da kungiyar ISIS ta yiwa dakarun sojin Najeriya a sansanin su wajen bayyana konannun gawawwakin su da kuma muhallai.

Majiyoyin rahoto da dama sun bayyana cewa, mayakan ISIS haye akan babura sun zartar da wannan mummunan hari ta hanyar harbin harsashin bindiga kan mai uwa da wabi da ya auku da misalin karfe 6.30 na Yammacin ranar Juma'a ta makon da ya gabata.

KARANTA KUMA: Boko Haram: Har yanzu akwai babban yanki a jihar Borno da ba a iya shiga - Osinbajo

Kungiyar masu tayar da kayar baya ta Boko Haram wadda ta zame jikin ta daga kungiyar ISIS a shekarar 2016, ta ci gaba da razanar da al'ummar Najeriya wajen zartar da ta'addanci cikin tsawon shekaru goma da kawowa yanzu rayukan kimanin mutane 30,000 sun salwanta.

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.android&pid=solomonovlink

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na dandalan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Ku fa'idantu da manhajar mu ta Azumi a wannan wata mai albarka a wannan shafi:

https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel