Innalillahi wa inna illaihi raji’un: Magaji Ubandoman Gombe ya rasu yana da shekara 80 a duniya

Innalillahi wa inna illaihi raji’un: Magaji Ubandoman Gombe ya rasu yana da shekara 80 a duniya

Wani babban jigon kasar kuma tsohon minister a jumhuriya ta biyu, Alhaji Magaji Mu’azu (Ubandoman Gombe) ya rasu a yammacin ranar Lahadi, 5 ga watan Mayu yana da shekaru 80 a duniya.

Ya rasu bayan yayi fama da jinya a babbar asibitin koyarwa ta tarayya da ke Gombe inda ya kwashe wasu watanni yana samun kulawar likitoci.

A cewar majiyoyi na iyalansa, za a yi sallar jana’izarsa a yau Litinin, 6 ga watan Mayu da misalin karfe 4:00 na rana a fadar sarkin Gombe.

An haifi marigayin a ranar 14 ga watan Maris, 1939 a Gombe, ya kuma rike manyan mukamaki a kasar.

Innalillahi wa inna illaihi raji’un: Magaji Ubandoman Gombe ya rasu yana da shekara 80 a duniya
Innalillahi wa inna illaihi raji’un: Magaji Ubandoman Gombe ya rasu yana da shekara 80 a duniya
Asali: UGC

A shekarar 1977, ya gaji mahaifinsa, marigayi Mu’azu Halilu a matsayin Ubandoman Gombe kuma babban jigo a masarautar Gombe.

KU KARANTA KUMA: Ramadan: Saraki ya bukaci Musulmai da su roki zaman lafiya da tsaro

Marigayin ya kuma kasance Shugaban jam’iyyar National Party of Nigeria (NPN) daga shekarar 1979 zuwa 1980 a lokacin jumhuriya ta biyu. A 1980, aka nada sa a matsayin a matsayin babban hadimin Shehu Usman Aliyu Shagari a jihar Gongola.

A 1983 lokacin da shugaba Shagari ya sake lashe zabe, sai aka nada Mu’azu a matsayin ministan tarayya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng