A karon farko tun kafuwar Najeriya, an samu 'sa hannun' mace a kan takardar Naira

A karon farko tun kafuwar Najeriya, an samu 'sa hannun' mace a kan takardar Naira

- An samu sa hannun mace a kan takaradar Naira, a karo na farko bayan kafuwar Najeriya, shekaru 59 da suka wuce

- Priscilla Ekwere Eleje, ita ce mace ta farko da ta taba 'sa hannu' a kan takardar Naira

- Ladi Kwali, ita ce mace ta farko da aka taba saka hotonta a jikin takardar Naira 20 (N20)

A karo na farko a tarihin Najeriya na shekaru 59 da wanzu wa, an samu 'sa hannun' mace, Priscilla Ekwere Eleje, a kan takardar Naira.

Hakan ya biyo bayan tabbatar da Eleje, mukaddashiyyar babban darektan kudi da gudanar wa a babban bankin kasa (CBN), a matsayin darekta.

Eleje, ita ce mace ta farko a tarinhin CBN, da ta taba rike mukamin, sannan mace ta farko da taba 'sa hannu' a kan takardar Naira.

A karon farko tun kafuwar Najeriya, an samu 'sa hannun' mace a kan takardar Naira
Takardar Naira
Source: UGC

Ladi Kwali, wata mata da ta kware wajen kera tukwanen tabo, ita ce mace ta farko da aka taba saka hotonta a jikin takardar Naira 20 (N20).

DUBA WANNAN: EFCC: Kotu ta yanke wa wasu 'yan N-power biyu hukuncin daurin shekara guda

'Yan cikin gida a CBN, sun shaida wa majiyar Legit.ng cewar gwamnan CBN, Godwin Emefieke, ya na kokari matuka wajen tabbatar da cewar mata sun samu wakilci a cikin babban bankin, musamman a manyan mukamai.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng