Zaben Gwamna: Jam'iyyar APC ta yi nasara a jihar Yobe

Zaben Gwamna: Jam'iyyar APC ta yi nasara a jihar Yobe

Da sanadin shafin jaridar The Cable mun samu cewa, dan takarar kujerar gwamnan jihar Yobe a karkashin inuwa ta jam'iyyar APC, Mai Mala Buni, ya lashe zaben gwamnan jihar Yobe kamar yadda hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta wato INEC ta zayyana.

Rahotanni sun bayyana cewa, Mai Mala Buni, ya lashe zaben jihar Yobe da kimanin kuri'u 444,013, inda ya lallasa abokin adawar sa na jam'iyyar adawa ta PDP, Umar Bello Iliya, da ya samu gamayyar kuri'u 95,703.

Mai Mala Buni
Mai Mala Buni
Asali: Original

KARANTA KUMA: Majalisar Jiha: APC ta lashe Kujeru 12, PDP ta samu 3 a jihar Kano

A jiya Lahadi jaridar Legit.ng ta ruwaito cewa, dan takarar kujerar gwamnan jihar Yobe a karkashin inuwa ta jam'iyyar APC, Mai Mala Buni, shine ke kan gaba yayin da ya lashe sakamakon zaben kananan hukumomi 9 na jihar Yobe.

Ga yadda sakamakon zaben gwamnan jihar Yobe ya kasance cikin wasu kananan hukumomi 9 kamar yadda hukumar INEC ta tabbatar.

Karamar Hukumar Damaturu

APC: 26,087

PDP: 3,760

Karamar Hukumar Bade

APC: 32,213

PDP: 8,854

Karamar Hukumar Karasuwa

APC: 24,263

PDP: 2,762

Karamar Hukumar Bursari

APC: 20,657

PDP: 2,813

Karamar Hukumar Gulani

APC: 21,765

PDP: 4,576

Karamar Hukumar Fika

APC: 36,519

PDP: 9,552

Karamar Hukumar Tarmuwa

APC: 11,338

PDP: 3,925

Karamar Hukumar Nangere

APC: 25,698

PDP: 4,765

Karamar Hukumar Gujba

APC: 17,714

PDP: 1,119

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na zaurukan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng