An kama jami’an INEC na bogi su 3 suna diban ma’aikata na wucin-gadi
- Rundunar yan sanda ta kama wasu jami’an INEC na bogi su 3 suna diban ma’aikata na wucin-gadi
- An bayyana sunayensu a matsayin Kaiyewu Folahan, Akintunde Ibukun da Azeez Kazeem
- An kuma gurfanar da masu laifin a gaban kotun Majistare, Yaba kan laifin, sojan gona, zamba, damfara da mallakar kayayyakin INEC ba bisa ka’ida ba
An kama wasu mutane uku a jiya a Yaba, jihar Lagas yayinda suke kokarin diban wasu jama’a a matsayin ma’aikatan wucin gadi na hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) na bogi.
Rundunar yan sanda ta bayyana wadanda aka kama a matsayin Kaiyewu Folahan, Akintunde Ibukun da Azeez Kazeem.
Kayayyakin da aka samu daga hannunsu a cewar yan sanda sun hada da, kwamfutar-tafi-da-gidanka, fam din diban ma’aikata na INEC Lagas guda 511 da hotunan fasfot a jiki.
Jami’in hulda da ama’a na rundunar yan sandan jihar Lagas, Chike Oti yace kamun ya biyo bayan wani korafi daga mataimakin daraktan INEC, a karamar hukumar Shomolu, Misis S.O. Akinwunmi, a ranar 22 ga watan Janairu cewa wasu mutane a shago mai lamba 33, Aluta Plaza, Federal College of Education, Akoka, na yi wa ma’aikatan INEC sojan gona sannan suna diban ma’aikatan wucin gadi.

Asali: Depositphotos
Oti yace bayan samun korafin, sai kwamishinan yan sandan jihar, Edgal Imohimi ya umurci ami’in dan sanda sashin ofishin yan sandan Pedro day a shiga sansanin mutanen tare da wasu jami’a. Hakan yayi sanadiyar kama su.
KU KARANTA KUMA: Ba zan yi sata ba, kuma ba zan bari kowa yayi sata ba – Buhari
Ya kara da cewa an gurfanar da masu laifin a gaban kotun Majistare, Yaba kan laifin, sojan gona, zamba, damfara da mallakar kayayyakin INEC ba bisa ka’ida ba.
Yace an garkame mutanen uku a gidan yari zuwa lokacin da za su cika ka’idar belinsu. An dage shari’an zuwa ranar 6 ga watan Afrilu, 2019.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT
Asali: Legit.ng