Ba zan yi sata ba, kuma ba zan bari kowa yayi sata ba – Buhari

Ba zan yi sata ba, kuma ba zan bari kowa yayi sata ba – Buhari

- Shugaban kasa Buhari ya sake jadadda alwashin da ya dauka na kin satar daga baitul malin kasar da kuma hana sauran mutane aikata hakan

- Buhari yace yan Najeriya za su iya bayar da shaidar cewa gwamnatinsa ta yi kokari sosai a wajen tattalin kudaden jama’a

- Ya ce sun samu gagarumin nasara a wajen ingnata tsaro, tattalin arziki da kuma yaki da cin hanci da rashawa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a jiya Laraba, 23 ga watan Janairu a Sokoto ya sake jadadda alwashin da ya dauka na kin satar daga baitul malin kasar da kuma hana sauran mutane aikata hakan.

Buhari ya sake ba yan Najeriya tabbacin cewa ba zai taba sata daga arzikinsu ba sannan kuma ba zai taba bari wani ya sace makomar kasar ba.

Ba zan yi sata ba, kuma ba zan bari kowa yayi sata ba – Buhari
Ba zan yi sata ba, kuma ba zan bari kowa yayi sata ba – Buhari
Asali: Facebook

Shugaban kasar yayi Magana a filin wasa na Giginya, wajen da aka gudanar da kamfen din neman tazarcensa a jiya, inda ya kara da cewa yan Najeriya za su iya bayar da shaidar cewa gwamnatinsa ta yi kokari sosai a wajen tattalin kudaden jama’a.

A cewarsa lokacin da ya ke kamfen din neman kuri’u a 2015, ya mayar da hankali, akan rashin tsaro, tattalin arziki da kuma yaki da cin hanci da rashawa, wanda ya kaddamar da gwamnatin tarayya a karkashin sa tayi matukar kokari.

KU KARANTA KUMA: INEC ta diba ma’aikatan wucin gadi 814,453 domin zabe

Akan nasararsa wajen yakar cin hanci da rashawa, Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara sannan tana ci gaba da jajircewa wajen yaki da rashawar.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng