Da duminsa: Ana can ana musayar wuta tsakanin sojoji da 'yan Boko Haram a Gaidam
Rahoton da muka samu na nuna cewa a halin yanzu mayakan kungiyar Boko Haram sun kai hari da garin Gaidam da ke jihar Yobe.
Mazauna garin sun shaidawa Daily Trust a yau Laraba cewa 'yan ta'addan sun shigo garin misalin karfe 5.30 na yamma inda suka rika harbe-harbe.
Wani dan garin ya ce 'yan ta'addan sunyi amfani da damar cewa yau ne ake cin kasuwan garin domin afkawa garin.

Asali: Twitter
DUBA WANNAN: Dino Melaye ya sake samun nasara a kan 'yan sanda a gaban Kotu
"Amma saboda sun sanar da mazauna garin cewa za su kawo hari, tuni sojojin Najeriya sun far musu," inji shi.
Ya ce a halin yanzu jiragen yaki masu saukan ungulu guda biyu sun iso garin domin taimakawa sojojin.
Ya ce a halin yanzu ana nan ana musayar wuta tsakanin sojojin da yan ta'addan.
Sai dai kawo yanzu, rundunar sojin na Najeriya ba ta fitar da sanarwa a kan lamarin ba.
Ku biyo mu domin samun karin bayani ...
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng