An lakada wa wani mutun duka bayan an kama shi yana cin burodi da kashi
- Wasu dandazon matasa sun lakada wa wani mutun dukan tsiya bayan kama shi yana cin burodi da kashin mutum
- Ana zargin da kasancewa mutumin mamba a cikin wata kungiyar asiri mai cin naman mutane
- Mutumin dai yayi tsirara ne a lokacin da yake cin burodi da kashin a sanyin safiya
Wasu dandazon matasa sun lakada wa wani mutun dukan tsiya bayan kama shi yana cin burodi da kashin dan adam a jihar Ekiti.
Jama’ar yankin da abin ya faru, sun shaida wa ‘yan sanda cewa, mutumin mamba ne a cikin wata kungiyar asiri mai cin naman mutane, abin da ya sa matasan suka kona wani sashi na jikinsa kafin daga bisani suka kashe shi har lahira.

Asali: Depositphotos
Rahotanni na cewa, wata tsohuwa ce ta fara gano mutumin wanda ya yi tsirara a yayin da yake cin burodi da kashin a sanyin safiyar ranar Litinin.
KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: NLC ta ki amincewa da N27,000 a matsayin mafi karancin albashi
Gabanin kashe shi, mutumin ya ambaci sunayen wasu limaman coci da ya ce yana da alaka da su, lamarin da ya sa gungun matasan kutsa cikin harabar wani coci domin neman daya daga cikin limaman, amma tuni ya ari na kare duk da dai an ce, an cafke shi a wata mahadar hanyoyi.
Tuni dai matasan suka rusa cocin da limamin ke jagorantar masu ibada.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng