Layukan waya sun karu zuwa 165m a watan Oktober - NCC

Layukan waya sun karu zuwa 165m a watan Oktober - NCC

Hukumar Sadarwa na Najeriya (NCC) ta ce adadin layyukan waya da 'yan Najeriya ke amfani dashi sun karu daga 162,058,918 a watan Satumba zuwa 165,239,443 a watan Oktoban shekarar 2018.

A cewar kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN), NCC ta bayar da wannan sanarwan ne a mujjalar wata-wata da take wallafawa a shafinta na yanar gizo a jiya Alhamis.

Punch ta ruwaito cewa hukumar ta ce layyukan wayoyin sun karu da 3,180,525 daga 162,058,918 da ake da su a watan Satumba.

Layukan waya sun karu zuwa 165m a watan Oktober - NCC
Layukan waya sun karu zuwa 165m a watan Oktober - NCC
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Yanzu-yanzu: An kara samun sansanin horon soji na bogi a jihar PDP

Rahoton ya ce a cikin layyukan wayan da ake amfani da su 165,239,443, tsarin GSM ya tantance 164,865,417 a watan Oktoba 2018.

Hakan na nuna cewa tsarin na GSM ya samu karin masu hulda da shi 3,179,670 a watan Oktoba idan a maimakon 161,685,747 da aka samu a watan Satumba.

NCC ta ce ana samun karuwar masu amfani da layyukan waya da 2.27% duba da cewa a Satumba ana da 115.76 amma a Oktoba an samu 118.03.

A wani rahoton, Legit.ng ta kawo muke cewa sojojin Najeriya sun gano sansanin horas da sojoji na bogi a Nonwa Gbam da ke karamar hukumar Tai na jihar Rivers.

Sai dai gwamnan jihar, Nyesom Wike ya zargi Hukumar Sojin Najeriya da yunkurin tayar da zaune tsaye a jihar inda ya ce 'yan banga jihar ke horas wa kuma tayi hadin gwiwa da 'yan sanda da wasu hukumomin tsaro kafin aka fara.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164