Girgizar kasa ta jikkata mutane 700 a kasar Iran

Girgizar kasa ta jikkata mutane 700 a kasar Iran

Rahotanni da ku zuwa mana sun nuna cewa akalla sama da mutane 700 ne suka jikkatta sanadiyar wata girgizar kasa mai karfin maki 6.3 da ta faru a kudancin kasar Iran a ranar Lahadi, shafin BBC Hausa ta ruwaito.

An tattaro cewa annoar girgiza ta fi kamari ne a lardin Kermanshah, inda a bara ma sama da mutane 600 ne suka mutu a wata mummunar girgizar kasa a tsawon shekara 10.

An jiyo motsin kasar a yankuna da dama na kasar, inda aka tattaro cewa akalla mutum guda ne ya rasa ransa a kusa da yankin Kurdistan na kasar Iraki.

Girgizar kasa ta jikkata mutane 700 a kasar Iran
Girgizar kasa ta jikkata mutane 700 a kasar Iran
Asali: Depositphotos

Sai dai babu rahotannin asarar rayuka a kasar Iran, kuma babu wani rahoto da ke cewa girgizar kasar ta yi wani babban ta'adi.

KU KARANTA KUMA: Dalilin da ya sa nake wayar wa da al’umma kai akan yaki da rashawa - Ganduje

Gwamnan lardin da abin ya shafa Houshang Bazvand ya ce: "Kimanin mutum 729 ne suka ji raunuka, 700 an yi musu magani har ma an sallame su...18 kuma an kwantar da su a asibiti."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng