Kwamitin sasanci na APC ta sanya ranar fara zama

Kwamitin sasanci na APC ta sanya ranar fara zama

Kwamitin sasanci da kawo zaman lafiya wanda uwar jam’iyyar All Progressive Congress, (APC)ta kafa a yankin arewa maso gabas karkashin jagorancin Gwamnan jihar Nasarawa, Alhaji Tanko Alhamakura ta fara aikin da aka sanya ta.

A wani jawabi dauke da sa hannun sakataren kwamitin, Mohammed Hassan Abdullahi, Esq, ya ce “kwamitin za ta kai ziyara ga dukkanin mambobin am’iyyar a jihohin arewa maso gabas musamman wadanda suka gudanar da zaben fidda gwwani na jam’iyyar da aka kammala da kuma basu fafutuka a tsari da sakamkon zaben sannan ta tattauna da su.

“Hakan na daga cikin kokarin jam’iyyar na magance dukkanin lamura da rigingimu da suka taso a jam’iyyar sanadiyar zaben fidda gwani.”

Kwamitin sasanci na APC ta sanya ranar fara zama
Kwamitin sasanci na APC ta sanya ranar fara zama
Asali: Depositphotos

Sanarwar ta kuma kara da cewa an shirya tattaunawa a Yobe da Borno a ranar Talata, 27 ga watan Nuwamba a gidan gwamnati, Maiduguri da misalin karfe 12 na rana.

KU KARANTA KUMA: Zabe: Yan siyasa na kwasar dalibai a matsayin yan bangan siyasa – Sarki Sanusi

Sannan na Buachi da Gombe za su biyo baya a ranar Laraba, 28 ga watan Nuwamba a masaukin bakin Command, Awalah Roundabout, Bauchi da misalin 12 na rana.

Sannan Adamawa da Taraba a ranar Alhamis, 29 ga watan Nuwamba a gidan gwamnati, Yola, da misalin karfe 12 na rana.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng