Yanzu Yanzu: Yan sanda sun tattara sun bar majalisar dokokin Akwa Ibom

Yanzu Yanzu: Yan sanda sun tattara sun bar majalisar dokokin Akwa Ibom

Yan sanda sun kawo karshen mamayar da suka kai majalisar dokokin jihar Akwa Ibom.

Tun a safiyar ranar Talata, 20 ga watan Nuwamba dai aka yiwa kofar shiga majalisar kawanya.

Sai dai an bude a yanzu yayinda yan sanda suka tattara suka bar harabar majalisar a yau Juma’a, 23 ga watan Nuwamba.

A ranar Laraba ne dai jami’an yan sanda suka mamaye wajen bayan wani rikici da ya barke a ranar Litinin.

Yanzu Yanzu: Yan sanda sun tattara sun bar majalisar dokokin Akwa Ibom
Yanzu Yanzu: Yan sanda sun tattara sun bar majalisar dokokin Akwa Ibom
Asali: Depositphotos

Kakakin majalisar, Onofio Luke ya kaddamar da kujerun yan majalisa biyar da suka sauya sheka daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) zuwa All Progressives Congress (APC), a kasuwa, larin day a sa yan iska hargitsa majalisan.

Daga bisani sai yan sanda suka rufe majalisar suka hana yan majalisa da ma’aikata shiga majalisan.

KU KARANTA KUMA: Za mu sadaukar da rayuwar mu don al’umman mu – Yan bangan Zamfara

Jim kadan haka sai majalisar dattawa ta yi umurni kan a binciki dalilin rufe majalisar, bayan Sanara Bassey Akpan mai wakiltan Akwa Ibom ta Arewa maso gabas ya tayar da zancen .

Sannan kuma a ranar Alhamis sai majalisar dattawa ta umurci yan sanda da su yi gaggawan barin majalisan.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng