Za mu sadaukar da rayuwar mu don al’umman mu – Yan bangan Zamfara
Sabbin mambobin yan tsaron sa kai wato Joint Task Force (CJTF) a Zamfara sun bayyana cewa za su sadaukar da rayuwar su domin kare al’umman su duk da hatsarin da ke tattare da yin hakan.
Wasu sabbin mambobin kungiyar da aka kwasa kwanan nan, wanda suka yi Magana don nuna jajircewarsu sun bayyana cewa a shirye suke da su kare garurwansu domin fitar da jihar daga matsalar yan fashi da makami.
Sun bayyana cewa suna sane da hatsarin da ke tattare da hakan amma a shirye suke don fuskantar kalubalen.

Asali: Depositphotos
“Za mu sanya rayuwar mu a kan hanya domin kare jihar mu. Ba za mu gaji a kudirinmu ban a don ganin mun fatattaki yan iskan da ke kaiwa kauyukan mu hare-hare ba,” cewar wani Musa Kabir.
KU KARANTA KUMA: Wata mata ta damfari dan majalisar wakilai N15m
Yace sun yanke shawarar kare mutanensu domin yin maganin yan fashi da makami da kuma barayn dabbobi da suka addabi jihar tsawon shekaru da dama ba tare da an dauki wani kwakwaran mataki ba akansu.
Wani dan kungiyar daga karamar hukumar Zurmi yace ba don sun shiga lamarin ba da a yanzu yan daba sun shafe kauyukan Zamfara da dama.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng