Yanzu Yanzu: Yan majalisar wakilai 2 sun sake barin APC

Yanzu Yanzu: Yan majalisar wakilai 2 sun sake barin APC

- Yan majalisar wakilai biyu sun sakesauya sheka daga jam'iyyar APC mai mulki

- Wadanda suka sauya shekar sune Ahmed Abu daga Jihar Niger da kuma Stephen Olemija daga Jihar Ondo

- Sun koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da kuma jam’iyyar Action Alliance

Mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) biyu a majalisar wakilai sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar mai mulki.

Idan za ku tuna a ranar Laraba, 21 ga watan Nuwamba ma wasu mambobi biyu suka bar APC.

Yanzu Yanzu: Yan majalisar wakilai 2 sun sake barin APC
Yanzu Yanzu: Yan majalisar wakilai 2 sun sake barin APC
Asali: Twitter

A zaman majalisar na yau Alhamis, 22 ga watan Nuwamba, kakakin majalisar, Yakubu Dogara ya karanta wasiku daga Ahmed Abu (Jihar Niger) da kuma Stephen Olemija (Jihar Ondo).

KU KARANTA KUMA: 2019: Masoya sun kawo karshen addu’o’in kwanaki 40 da suka yi wa Buhari (hotuna)

Sun kuma bayyana komawarsu jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da kuma jam’iyyar Action Alliance.

A wani lamari na daban, mun ji cewa Gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima ya bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kokari don ganin ta kawo jihohi 30 a zaben 2019.

Ya bayyana hakan a ranar Laraba, 21 ga watan Nuwamba lokacin shugaban jam’iyyar APC na kasa, Kwamrad Adams Oshiomhole ya kaddamar da kwamitocin sulhu domin magance matsalar zaben fidda gwani da ya addabi jam’iyyar a fadin kasar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng