2019: Kada a ji komai za mu kawo wa APC Sokoto - Wamakko
Shugaban kungiyar sanatocin arewa, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya yi hasashen cewa cikin rowan sanyi jam’iyyar All Progressives Congress (APC) za ta lashe zabe a Sokoto, yayinda yake yaba ma tarin goyon bayan da jam’iyyar ke samu a dukkan matakai na kasar.
Sanata Wamakko, ya yi Magana ne a gidansa na Gawon Nama, da ke Sokoto lokacin da yake jawabi ga taron jiga-jigai da mambonbin jam’iyyar jim kadan bayan dawowarsa daga wani ziyarar aiki a Abuja.
Da yake Magana akan zaben 2019, Wamakko ya bayyana cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari da dukkanin yan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), za su lashe zabe mai zuwa.

Source: Depositphotos
Wamakko ya kuma bayyana cewa jam’iyyar da yan takaranta a dukka matakai ba za su ba yan Najeriya kunya ba kuma za su cika alkawaransu.
Ya kuma yi kira ga magoya bayan jam’iyya da su guji duk wani tashin hankali da hayaniya a lokaci da bayan zabe.
KU KARANTA KUMA: Karancin albashi: N30,000 bai yi yawa ba don haka ku biya – Sanata Ndume
A wani lamari na daban, tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Abdusalami Abubakar ya bayyana cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kawo zaman lafiya a kasar ta hanyar amsar sakamakon zaben shugaban kasa na 2015 wanda ya sha kasa.
A cewarsa kasar Najeriya bata san irin godiyar da za ta yiwa Jonathan ba bisa wannan karamci da dattako da ya nuna.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng