Yanzu Yanzu: Kotu ta haramta wa Daily Nigerian wallafa bidiyon cin hanci na Ganduje

Yanzu Yanzu: Kotu ta haramta wa Daily Nigerian wallafa bidiyon cin hanci na Ganduje

Wata babbar kotun Kano ta yi na’am da karar da gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya shigar da ke neman a haramtawa jaridar Daily Nigerian da Jafaar Jafaar, mawallafinta, wallafa bidiyo a game da shi.

The Cable ta ruwaito cewa kafar watsa labaran ta wallafa wasu bidiy da ke nuna Ganduje yana karban cin hanci daga hannun yan kwangila.

Legit.ng ta tattaro cewa Ganduje ya nemi jaridar ta biya shi naira biliyan 3 akan bidiyon.

Yanzu Yanzu: Kotu ta haramta wa Daily Nigerian wallafa bidiyon cin hanci na Ganduje
Yanzu Yanzu: Kotu ta haramta wa Daily Nigerian wallafa bidiyon cin hanci na Ganduje
Asali: Depositphotos

Da take yanke hukunci a ranar Litinin, 19 ga watan Nuwamba, kotu ta haramta wa Jafaar da Daily Nigerian wallafa ko yada bidiyon gwamnan har zuwa lokacin da za’a sake zama a ranar 6 ga watan Disamba.

KU KARANTA KUMA: Buhari, Obasanjo, Atiku za su hade wajen kaddamar da littafin Jonathan a gobe

A baya mun ji cewa dan kwangilar daya baiwa gwamnan jahar Kano Abdullahi Umae Ganduje tare daukansa bidiyoya bayyana cewa a shirye yake ya gurfana gaban majalisar dokokin jahar Kano don zube musu hujjjojinsa game da sahihancin wannan bidiyo.

Majiyar Legit.com ta ruwaito dan kwangilar da bai bayyana sunansa ba ya bayyana ma majalisar burinsa na gurfana a gabansu ne cikin wata wasika da lauyansa Saeed Twada ya kai ma majalisar kafa da kafa, inda yace shi ne ya dauki Ganduje hoton, don haka yace akwai bukatar Ganduje ma ya bayyana.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng