Zaben maye gurbi a Kwara: Dan takarar PDP ya fadi akwatinsa
A yau ne hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ke gudanar da zaben maye gurbi wasu kujeru daban-daban a jihohin Bauchi, Katsina, Kwara da Kuros Riba.
Rahotanni sun bayyana cewar ma su zabe a jihar Kwara sun fito kwan su da kwarkwata domin kada kuri'a a zaben maye gurbin majalisar wakilai a mazabun Ekiti/Irepodun/Isin/Oke-Ero.
A mazabar Oro ta 2, inda ministan yada labarai na kasa, Alhaji Lai Mohammed, ya kada kuri'ar sa, ga yadda sakamakon zaben ya kasance;
APC 138
PDP 49
A wani sakamakon kuma da aka saki, dan takarar jam'iyyar PDP ya fadi akwatinsa a mazabar sa. Ga sakamakon:
Igangu Alatise
APC 120
PDP 80
Ba hukumar zabe mai zaman kanta ce ta bayyana wannan sakamako ba.
KU KARANTA: Ban taba karbar albashi ba tunda na hau kujerar gwamna - Gwamnan APC
Za mu cigaba da kawo sakamakon...
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng