Buhari na ganawar sirri da shugban kasar Guinea Bissau

Buhari na ganawar sirri da shugban kasar Guinea Bissau

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis, 15 ga watan Nuwamba ya yi ganawar sirri da shugaban kasar Guinea Bissau, Jose Mario Vaz a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Legit.ng ta tattaro cewa Shugaba Vaz ya iso fadar shugaban kasa da karfe 11 na safe sannan ya samu tarba daga shugaba Buhar wanda ya kai shi ofishin sa kai tsaye sannan a take suka fara ganawa.

Buhari na ganawar sirri da shugban kasar Guinea Bissau
Buhari na ganawar sirri da shugban kasar Guinea Bissau
Asali: Facebook

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dawo gida Najeriya bayan ziyarar aiki da ya kai Paris, kasar Faransa na kwanak biyar.

KU KARANTA KUMA: Yawancin hanyoyin Najeriya sun tashi aiki - FERMA

Shugaban kasar ya dawo gida a ranar Laraba, 14 ga watan Nuwamba. Ya hadu da Gwamna Aminu Bello Masar na Katsina, Gwamna Kayode Fayemi na Ekiti da Gwamna Willie Obiano na Anambra.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel