Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi

Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi

Biyo bayan kisan gilla da aka yiwa dan jaridan kasar Saudiyya, Jamal Khashoggi, an yankewa mutane biyar da ake zargi da hannu a kisan dan jaridan a kasar Istanbul, kasar Turkiyya.

Daily Mail ta ruwaito cewa dan sandan da ke gabatar da kara ya kuma sanar da tuhume-tuhumen da ake yi wa mutanen shida da ake zargi da hannu a kisan.

Legit.ng ta rahoto cewa dan sandan mai kara yace Saudiyya ta yarda cewa anyi wa Khashoggi wani allura na mutuwa a ofishin jakadancin kasar a ranar 2 ga watan Oktoba.

Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi
Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi
Asali: Depositphotos

A baya mun ji cewa Kasar Saudia ta bayyana cewa zata biya diyyar dan jarida daya rasa ransa a lokacin da yake ziyartar ofishin jakadancin kasarsa a Turkiyya.

KU KARANTA KUMA: Madalla! An kori jami'an Kwastam 28 masu hannu kan shigowa da muggan makamai

A yayin wata tattaunawa da CNN tayi da iyalan mamacin Salah da Abdallah sunce a dawo musu da gawar mahaifin su domin a binneshi a kasar sa wato Medina dake kasar Saudi Arabia, sannan sunce sun yadda da sarki Salman akan kokarin binciko wadanda sukayi wannan aika aika don a hukuntasu.

Wannan nuna rashin tausayi na kashe Kashoggi ya taba shugaban cin sarkin na Saudia.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng