Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi

Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi

Biyo bayan kisan gilla da aka yiwa dan jaridan kasar Saudiyya, Jamal Khashoggi, an yankewa mutane biyar da ake zargi da hannu a kisan dan jaridan a kasar Istanbul, kasar Turkiyya.

Daily Mail ta ruwaito cewa dan sandan da ke gabatar da kara ya kuma sanar da tuhume-tuhumen da ake yi wa mutanen shida da ake zargi da hannu a kisan.

Legit.ng ta rahoto cewa dan sandan mai kara yace Saudiyya ta yarda cewa anyi wa Khashoggi wani allura na mutuwa a ofishin jakadancin kasar a ranar 2 ga watan Oktoba.

Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi
Yanzu Yanzu: Saudiyya za ta gille kan mutane 5 dake da hannu a mutuwar Jamal Khashoggi
Asali: Depositphotos

A baya mun ji cewa Kasar Saudia ta bayyana cewa zata biya diyyar dan jarida daya rasa ransa a lokacin da yake ziyartar ofishin jakadancin kasarsa a Turkiyya.

KU KARANTA KUMA: Madalla! An kori jami'an Kwastam 28 masu hannu kan shigowa da muggan makamai

A yayin wata tattaunawa da CNN tayi da iyalan mamacin Salah da Abdallah sunce a dawo musu da gawar mahaifin su domin a binneshi a kasar sa wato Medina dake kasar Saudi Arabia, sannan sunce sun yadda da sarki Salman akan kokarin binciko wadanda sukayi wannan aika aika don a hukuntasu.

Wannan nuna rashin tausayi na kashe Kashoggi ya taba shugaban cin sarkin na Saudia.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel