Ku daina amfani da matasa a matsayin Karen farauta – Obasanjo ga yan siyasa

Ku daina amfani da matasa a matsayin Karen farauta – Obasanjo ga yan siyasa

- Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, a ya gargadi yan siyasa a Najeriya akan amfani da matasa a matsayin Karen farauta

- A cewarsa su suna killace yaransu a tsararren wuri da makarantu sannan su yi amfani da yaran talaka wajen ta da zaune tsaye

- Obasanjo ya marawa gyara kundin tsarin mulkin baya wanda ya ba matasa damar shiga harkar siyasa

Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo, a jiya, Laraba, 14 ga watan Nuwamba ya gargadi yan siyasa a Najeriya akan amfani da matasa a matsayin Karen farauta, yayinda suke boye nasu ‘ya’yan a killataccen wuri.

A wata sanarwa a Abeokuta daga hadiminsa, Kehinde Akinyemi, tsohon shugban kasar yayi mgana a birnin Landan wajen kaddamar da kwalejin King’s College London Global Leaders Engagement Series.

Ku daina amfani da matasa a matsayin Karen farauta – Obasanjo ga yan siyasa
Ku daina amfani da matasa a matsayin Karen farauta – Obasanjo ga yan siyasa
Asali: Instagram

A cewarsa: “Ya ishe ku yin amfani da yayan mutane a matsayin Karen farauta yayinda muke killace namu a aljannah.

"Ya ishe ku amfani da yayan mutane a matsayn masu kwato akwatunan zabe, yayinda namu ke tsadaddun makarantu."

KU KARANTA KUMA: Mutanen Najeriya na neman Kasar Amurka ta binciki Atiku kafin zaben 2019

Tsohon shugaban kasar ya marawa gyara kundin tsarin mulkin baya wanda ya ba matasa damar shiga harkar siyasa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng