Hukumar Hisbah za ta kama masu rawar fadi ka mutu a Kano

Hukumar Hisbah za ta kama masu rawar fadi ka mutu a Kano

Hukumar Hisbah reshen jihar Kano ta sanar da cewar jami’an ta za su fara kama duk mutumin da aka sama yana taka sabuwar rawar nan ta 'fadi ka mutu' wanda ke tashe a yanzu.

A ranar Talatar da ta gabata ne wani bidiyo ya fito inda aka nuno wasu 'yan mata sanye da hijabi na tikar rawar da ta samo asali daga kasar Afirka ta Kudu.

Wasu mutane sun ce 'yan matan da ke cikin bidiyon 'yan jihar Kano ne, amma kakakin hukumar Hisbah a Kano, Adamu Yahaya ya shaida wa majiyarmu ta BBC Hausa cewa ba su samu wani rahoto makamancin wannan ba.

Hukumar Hisbah za ta kama masu rawar fadi ka mutu a Kano
Hukumar Hisbah za ta kama masu rawar fadi ka mutu a Kano
Asali: UGC

Wannan sabuwar rawar ta samo asali ne daga wata waka da mawakin Afirka ta Kudu, King Monada, ya rera mai suna 'Maldwedhe' da aka ce tana caza kwakwalwar matasa.

KU KARANTA KUMA: Rundunar soji ta karyata batun hana shige da fice a Maiduguri

Ma'anar kalmar Maldwedhe ita ce cuta, kuma Monada ya yi amfani da kalmar ce dangane da wani maras lafiya da ke dauke da cutar wadda ke sa shi ya suma idan ya kama masoyiyarsa tare da wani.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng