Fafutukar da muke yi tsakanin nagari da mugu ne – Osinbajo

Fafutukar da muke yi tsakanin nagari da mugu ne – Osinbajo

Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa fafutukar da ake yi a Najeriya tsakanin nagari da mugu, sannan kuma cewa ba tsakanin manyan addinan kasar biyu bane.

A cewar wata sanarwa daga babban mai bashi shawara a affin labarai , Mista Laolu Akande a ranar Lahadi, 11 ga watan Nuwamba, mataimakin shugaban kasar yayi jawabi a wani taro da kungiyar manyan malamai, reshen Ikeja, jihar Lagas suka shirya a ranar Asabar.

Ya shawarci shugabannin addinin da su ci gaba da fada ma mabiyansu cewa su rungumi zaman lafiya sannan su yi aiki don hadin kan kasar.

Osinbajo ya ce takatsantsan da gwamnatin nan ke yi wajen kashe kudi ya taimaka matuka wurin cimma nasara wajen yin ayyukan ci gaba fiye da na gwamnatocin baya.

Fafutukar da muke yi tsakanin nagari da mugu ne – Osinbajo
Fafutukar da muke yi tsakanin nagari da mugu ne – Osinbajo
Asali: Facebook

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin ta zuba jari sosai wajen kare al’umma, inda tace wannan ne mafi girma da ya taba faruwa a tarihin kasar.

KU KARANTA KUMA: Rigimar APC ta kara cabewa a Ondo bayan ‘Yan Majalisa sun yi watsi da zama da Gwamna

Mataimakin shugaban kasar ya kuma lissafa ayyukan ci gaba wanda suka hada da aikin jirgin kasa na Lagas-Kano, hanyar moota biyu na Lagas-Ibadan da kuma gadar Niger na biyu.

Ya kuma yi bayanin cewa ta shirin N-Power kadai matasa 500,000 ne suka amfana.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng