Me yasa OakTV ke baiwa Ministan sadarwa hakuri kan tonon ko nawa wai ake kashewa El-Zakzaki?

Me yasa OakTV ke baiwa Ministan sadarwa hakuri kan tonon ko nawa wai ake kashewa El-Zakzaki?

- Gidan talabijin na Oak ya nemi afuwar want minista

- Gwamnati tana kashe N 3.5m wajen ciyar da Alzakzakiy a wata

- Muna neman afuwa sannan munyi nadamar wannan abu

Me yasa OakTV ke baiwa Ministan sadarwa hakuri kan tonon ko nawa wai ake kashewa El-Zakzaki?
Me yasa OakTV ke baiwa Ministan sadarwa hakuri kan tonon ko nawa wai ake kashewa El-Zakzaki?
Asali: UGC

Gidan talabijin na OAK ya nemi afuwar ministan watsa labarai Lai Muhammed a bisa wani bidiyo daya watsa inda ministan ya bayyana cewa gwamnati tana kashe makudan kudade wajen ciyar da Alzakzakiy wanda yake daure tun a shekara ta 2015.

Amma abin mamaki a ranar Alhamis wannan bidiyo ya fara yawo a kafafen sadarwa.

A wasikar ban hakuri da gidan talabijin din ya turawa ministan sunce*" A ranar Laraba 7 ga Nuwamba 2018 gidan talabijin dinmu ya samu tangarda a bangaren hira da muka gudanar da ministan watsa labarai ".

Muna neman afuwa da kuma yafiya a bisa wannan kuskure.

Bidiyon yana dauke da ministan ne a lokacin da yake wasu bayanai akan Alzakzakiy.

DUBA WANNAN: An sace injin saukar jirgi a Iyapot

Inda yake cewa "Anata neman inda zakzakiy yake to yana nan kuma ana ci dashi."

"Gwamnati tana kashe N3.5m a wajen ci dashi a wata".

Inda Ministan tafiye tafiye Rotimi Amaechi ya katse shi ta hanyar ce masa "in kuwa haka ne shima zaizo su kamashi".

Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng

Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng