Yadda alluran rigakafi ke ceton Najeriya da ma rage mata asarar kudi
- Najeriya ta ceci biliyoyi akan harkar riga kafi
- Za'a fara gudanar da aikin a kananan hukumomi 6
- Ya kamata mu dage wajen kawo karshen wadannan cututtuka
Hukumar lafiya ta duniya watau WHO, ta bakin wata ma'aikaciyar ta Dr Larai Aliyu Tambuwal tace Najeriya ta tanaji biliyoyin kudade dan bada kariya sanadiyyar cuttuttukan da ake fama dasu.
Za'a fara gudanar da wannan aiki ne a wasu kananan hukumomi 6 dake kasar nan a ranar 8 ga watan Nuwamba zuwa Disemba.
Dr. Tambuwal a lokacin da take wannan bayani a Sokoto tace jihar ta Sokoto bata daga cikin jihohin dake da karancin RI da SIAs.
DUBA WANNAN: N35m muke kashe wa Azzazzaki a wata daya
Ya zama tilas mu nemi hanyar kawo kariya daga kamuwa da wadannan cutukan.
Anan jihar Sokoto bamu kara samun wannan matsalar ba tun akan Abubakar Ibrahim dan shekaru 10 wanda yayi fama da shanyewar barin jiki tun a shekara ta 2012.
Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng