Tashin hankali a Kaduna yayinda yan sanda suka kama mutum 32 kan sabon rikici

Tashin hankali a Kaduna yayinda yan sanda suka kama mutum 32 kan sabon rikici

Rundunar yan sanda a jihar Kaduna sun kama mutane 32 da ake argi da hannu a sabon rikicin da ya barke a jihar.

A wata sanarwa daga kakakin gwamnan jihar, Samuel Aruwan ya bayyana cewa jami’an tsaro sun dakatar da wani yunkuri na tayar da zaune tsaye a wuraren ibada da ke unguwannin Hayin Banki da kuma Kawo a cikin garin Kadunan.

Har ila yau an kuma kashe mutum daya a Kasuwan Magani kana aka kama wani mutum da tsakar dare dauke da bindiga, in ji sanarwar.

Tashin hankali a Kaduna yayinda yan sanda suka kama mutum 32 kan sabon rikici
Tashin hankali a Kaduna yayinda yan sanda suka kama mutum 32 kan sabon rikici
Asali: Depositphotos

Mista Aruwan ya ce "za a gudanar da bincike kan mutanen sannan a gufrfanar da su gaban kuliya."

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Shugaban APC a Enugu ya tsallake rijiya da baya yayinda makasa suka harbi mai tsaronsa

A halin da ake ciki, gwamnatin jihar ta ce ta sassauta dokar hana fita a yankin Kachia inda a ranar Asabar, 27 ga watan Oktoba za a bar mutane su fita har zuwa karfe biyar na yamma.

Sannan kuma daga ranar Lahadi za su fita daga karfe shida na safe zuwa biyar na yammaci a kullum.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng