2019: Duk mai korafi ya hakura, mun gama fidda masu mana takara - APC ga masu koken wariya
- Jam'iyar APC tace an samu hargitse ne sanadiyyar bawa yan takara suyi karamin zabe
- Ya bayyana haka ne a karamin zaben gwamnoni a jahar Ogun
- Sanata Shehu Sani yabar APC

Asali: Depositphotos
Jam'iyar APC ta bayyana a jiya cewa ana samun wannan hargitsin ne sanadiyyar bawa masu takara suyi karamin zabe da za'a gudanar a shekara mai zuwa.
Mai magana da yawun jam'iyyar kan batun zaben cikin gidan na gwamnoni da aka gudanar a jahar Ogun da Imo yace INEC ta riga ta karbi sunaye, kuma ta rufe karbar musaya.
Da kuma zaben sanatoci da akayi a Kaduna da Enugu sannan da jerin yan takarkaru da jahar Zamfara ta mikawa hukumar zabe ta INEC.
DUBA WANNAN: Sarki Salman zai iya sauke Yarima bin Salman daga mai-jiran Gado
A jihar Kaduna sanata Shehu Sani yabar APC ya koma PRP bayan cire sunan sa da jam'iyar tayi a cikin jerin yan takara.
A jihar Enugu kuma Darakta Janar Osita Okechukwu ya kaiwa National chairman Adams Oshiomhole caccaka bayan ya hana shi takara.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng