Dalilin da ya sa muka dakatar da tattakin yan shi’a a Kano – Yan sanda

Dalilin da ya sa muka dakatar da tattakin yan shi’a a Kano – Yan sanda

Rundunar yan sandan jihar Kano ta nemi mabiya kungiyar Shi’a da su sauya tattakin da suka shirya yi.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kakakin rundunar yan sandan, Magaji Musa Majia, ya bayyana a ranar Alhamis,25 ga watan Oktoba cewa kungiyar ta sanar da hukumar shirinsu na taruwa a Gyadi-Gyadi kan Gadar Lado don fara tattakin su na 'arbaeen'.

Legit.ng ta tattaro cewa Majia ya ce an kin amincewa da bukatar nasu saboda wajen da suka nemi yin taron ba masallaci bane sai ya kasance babban mashigin Kano daga hanyoyin Zaria da Maiduguri.

Dalilin da ya sa muka dakatar da tattakin yan shi’a a Kano – Yan sanda
Dalilin da ya sa muka dakatar da tattakin yan shi’a a Kano – Yan sanda
Asali: Depositphotos

A cewarsa duk wani taro a wannan waje zai haifar da cunkoso da rashin walwala a tsakanin jama’a.

KU KARANTA KUMA: Fayose ya gaza cika ka’idojin belin da kotu ta gindaya

Ya ce indai a masallaci ne inda babu wanda zai takura an basu izinin udanar da hakan amma indai a Gadar Lado ne toh babu halin yin hakan.

A wani lamari na daban mun ji cewa Gwamnatin jihar Kaduna ta sake mayar da dokar hana fita na sa’o’i 24 a birnin Kaduna da kewayenta, Kasuwan Magani, Kajuru, Kateri da kuma Kachia.

Wannan doka zai fara aiki ne daga karfe 11 na safiyar yau Juma’a, 26 ga watan Okotoba har illa-ma-shaa’a.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng