Har yau ba mu da dan takarar gwamna a Jihar Imo –APC

Har yau ba mu da dan takarar gwamna a Jihar Imo –APC

Kakakin Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, Lanre Issa-Onilu, ya caccaki masu shirya munakisa don ganin tsige shugaban jam’iyyar, Adams Oshimhole.

Ya bayyana wasu gwamnoni da manyan jami’an gwamnatin da suka bukaci hakan a matsayn masu son zucia cewa suna yi ne kawai don ba su yi nasara ba a zaben fidda gwani, ko kuma a ce jama’a ba su zabi san ransu ba.

Da ya ke hira da yan jarida, Lanre ya ya caccaki wasu gwamnoni, musamman na jihar Ogun, Ibikunle Amosun, wanda ya kira Oshiomhole ‘dan gada-gada.’

Har yau ba mu da dan takarar gwamna a Jihar Imo –APC
Har yau ba mu da dan takarar gwamna a Jihar Imo –APC
Asali: Depositphotos

Hakazalia ya soki shugaban gidan radiyon Najeriya da ya ambaci Osinajo a matsayin dan damfara.

Da ya ke magana a kan dan takarar gwamnan APC a jihar Imo, inda ake zargin Gwamna Rochas Okorocha ya yi karfa-karfa da banga-bangar dora sirikin sa, Uche Nwosu, Lanre ya ce har yau APC ba ta kai ga yanke hukuncin wane ne dan takarar gwamna a jihar Imo ba tukunna.

KU KARANTA KUMA: Akwai makircin da ake kullawa akan Buhari - Amosun

Ya yi nuni da cewa ranar 2 ga watan Nuwamba ne wa’adin mika wa INEC sunan dan takarar gwamna a kowace jiha zai cika, ba ranar 18 ga watan Oktoba kamar yadda INEC din ta rika jaddadawa ba.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Lagit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng