Akwai makircin da ake kullawa akan Buhari - Amosun
Gwamnan jihar Ogun, Ibikunle Amosun ya yi zargin cewa akwai wani makircin da mutanen da suka yi kane-kane a jam’iyyar All Progressives Congress (APC)ke kullawa domin kwancewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zani a kasuwa.
A wata sanarwa dauke da sa hannunsa a daren ranar Talata, Amosun yace masu kulla masa sharri suna harin Buhari ne.

Asali: UGC
Ya ce alakar sa da shugaban kasar na nan daram-kadam da karfi duk da kokarinda masu adawa ke yin again sun shiga tsakaninsu ta hanyar sakin zantuan farfaganda.
KU KARANTA KUMA: Bidiyon cin hanci: Abunda Jaafar ya yi ba zai hana mu zabar Ganduje ba – Yaran makaranta
Amosun ya karyata duk zarge-zargen da aka yiwa Buhari wanda aka alakanta dashi inda ya bayyana su a matsayin karya mara tushe.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Lagit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng