Duk lokacin da nayi kokarin sallaman wani mai laifi, shugabannin addini su ka nemi hana ni - Osinbajo

Duk lokacin da nayi kokarin sallaman wani mai laifi, shugabannin addini su ka nemi hana ni - Osinbajo

Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya ce a duk lokacin da zai sallami wani jami’in gwamnati da aka kama da laifin sata, sai shugabannin addini da na siyasa da dama su nemi da kada yayi hakan.

Da yake magana a taron kwamitin tattalin arzikin Najeriya kan rashawa da doka a Abuja a ranar Litinin, 22 ga watan Oktoba, mataimakin shugaban kasar yace shugabannin Najeriya kan toshe hanya a duk lokacin da za’a yaki cin hanci da rashawa.

Naire Woods, gidauniyar Blavatnik School of Government a jami’ar Oxford, wadanda suka jagoranci taron sun bukaci Osinbajo da ya fada ma taron wanda ke kiran shi a lokacin da yayi yunkurin sallaman mai laifi.

Duk lokacin da nayi kokarin sallaman wani mai laifi, shugabannin addini su ka nemi hana ni - Osinbajo
Duk lokacin da nayi kokarin sallaman wani mai laifi, shugabannin addini su ka nemi hana ni - Osinbajo
Asali: Depositphotos

A nashi martanin Osinbajo yace: “Zan so nayi Magana kan shugabannin Najeriya, kuma bai dace mutun ya kasance mai fadada zance ba, abode mutanen da ked a hanyar ganinka kai tsaye na iya kasancewa shugabannin siyasa, shugabannin addini, manyan yan kasuwa, duk ma wanda ked a alaka da kai.

“Akwai wani tsari inda mutane za su iya ganin, ‘mai zai hana ka kyale wane na dan lokaci?’wanda hakan wata matsala ne na daban. Ba kira daya ba, kira da dama.”

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Fusatattun ma’aikata sun tsare dakataccen sakataren NHIS a ofishinsa (hotuna)

Mataimakin shugaban kasar yace gwamnati na aiki sosai don ganin ta magance lamarin cin hanci da rashawa inda ya bayyana cewa tun daga lokacin da ya zama mataimakin shugaban kasa, ya bayar da gudunmawa sosai wajen magance cin hanci da rashawa kuma abun ya zarce tunanin sa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng