Zargin sata: An taso tsohon Gwamnan Edo Adams Oshimhole a gaba
Kwanakin baya ne wani babban Fasto mai kare hakkin Bayin Allah marasa karfi kuma babban ‘Dan gwagwarmaya a Kudancin Najeriya watau Osadolor Ochie ya shigar da Adams Oshimhole Kotu.

Asali: Depositphotos
Osadolor Anthony Ochie ya maka Shugaban na Jam’iyyar APC mai mulki da kuma Hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ne a wani babban Kotun Tarayya da ke zama a Birnin Tarayya Abuja kwanaki.
Rikakken ‘Dan gwagwarmayan ya shiga da EFCC Kotu ne a dalilin watsi da binciken da aka nemi tayi a kan tsohon Gwamnan Jihar Edo Adams Oshiomhole. An shigar da korafin zargin satar da ke kan Gwamnan amma EFCC tayi gum.
KU KARANTA: Fitaccen Sanatan APC ya koka da kashe-kashen da ake yi a kasar nan
Bishof Osadolor Ochie yace yana da hujjoji da ke nuna irin mahaukaciyar satar da Adams Oshiomhole yayi a lokacin yana Gwamna don haka yake neman a bincike sa. Ganin EFCC tayi kunnen kashi ne ya shiga Kotu da kan sa.
Ochie wanda Malamin addini ne, ya kai karar tsohon Gwamnan na APC ne ta hannun wani Lauya Dr. Ehiogie West Idahosa wanda yanzu an kuma fara yi masu yadda su ke so. Ochie dai ya bayyana cewa ba ya tare da wata Jam’iyyar siyasa.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng