Bidiyon cin hanci: Majalisar dokokin jihar Kano ta aika sammaci ga editan Daily Nigerian

Bidiyon cin hanci: Majalisar dokokin jihar Kano ta aika sammaci ga editan Daily Nigerian

Kwamitin da majalisar dokokin jihar Kano ta kafa domin binciken ingancin bidiyon da ke nuna Gwamna Abdullahi Ganduje na karban rashawa ya aika sammaci ga babban editan Daily Nigerian, Malam Ja’afar Ja’afar da ya gurfana a gaban ta.

Jaridar Daly Nigerian c eta wallafa bidiyon wanda ya haifar da kace-nace.

Sakataren kwamitin, Nujtafa Aminu ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) a Kano a ranar Juma’a, 19 ga watan Oktoba.

Bidiyon cin hanci: Majalisar dokokin jihar Kano ta aika sammaci ga editan Daily Nigerin
Bidiyon cin hanci: Majalisar dokokin jihar Kano ta aika sammaci ga editan Daily Nigerin
Asali: Depositphotos

Aminu ya ce kwamitin a wasika mai kwanan wata 19 ga Oktoba ta bukaci Ja’afar day a gurfana a gabanta a ranar Alhamis, 26 ga watan Oktoba a zangon majalisar.

KU KARANTA KUMA: Majalisar dattawa ta bukaci EFCC da ta binciki badakallar hukumar aikin Hajji

Ya ce an samar da ingantaccen tsaro don bad an jaridan kariya yayinda ake sanya ran zai amsa wasu tambayoyi kan bidiyon day a saki a yanar gizo.

A cewarsa, kwamitin ta rigada ta ziyarci kwamishinan yan sandan jihar, Mista Rabi’u Yusuf da daraktan yan sandan DSS domin neman goyon bayansu da tsaro.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta NAIJ.com Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.naij.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng