Da duminsa: Bayan gano motar sa, sojoji sun kama wani mutum sanye da kakin janar Alkali, hoto

Da duminsa: Bayan gano motar sa, sojoji sun kama wani mutum sanye da kakin janar Alkali, hoto

Bayan nasarar gano motarsa a wani tafin ruwa mai zurfin gaske dake unguwar Dura Du a karamar hukmar Jos ta Kudu, rundunar soji dake neman Manjo Janar Idris Alkali (mai ritaya) da ya bace tayi nasar cafke wani mutum sanye da kakin janar din.

A jiya ne Legit.ng ta kawo maku rahoton cewar hukumar sojin Najeriya ta gano motar Janar (mai ritaya) a karkashin wani kududdufi dake unguwar Dura Du a karamar hukumar Jos ta kudu, bayan fiye da sati uku ana nemansa.

Manjo Janar Idris Alkali ya bace ne tun ranar 3 ga watan Satumba a hanyarsa ta zuwa Bauchi daga Abuja. Rahotannin da hukumar soji ta tattara sun gano cewar Alkali ya bata ne a karamar hukumar Jos ta kudu.

Da duminsa: Dakarun soji sun kama wani mutum da kakain Janar Idris Alkali, hoto
Mutumin da aka kama da kakain Janar Idris Alkali
Asali: Facebook

Babu tabbacin ko gawar Alkali na cikin motar. Sai dai Birgediya Janar Umar Mohammed, shugaban rundunar soji dake farautar neman inda Janar din yake, ya bayyana cewar zasu kwashe ruwan domin tabbatar da gawar Alkali na ciki ko akasin haka.

DUBA WANNAN: Hukumar sojin sama ta bude katafaren dakin binciken laifuka na kimiyya, hotuna

Tun a ranar 20 ga wata ne, Birgediya Janar Umar Mohammed, shugaban tawagar masu neman Janar Alkali, ya shaidawa gidan talabijin na Channels a yau, Alhamis, cewar sun tura rundunar soji zuwa yankin Dura Du dake karamar hukumar Jos ta kudu a jihar Filato.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng