Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)

Tun bayan da Shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi takawar mita 800 daga masallaci zuwa gidansa a lokacin bkin babban Sallah, mutane tare da yan siyasa na ta tofa albarkatun bakunansu.

Wasu yan siyasa na ganin zasu iya bjintar da ta fin a shugaban kasar yayinda wasu suka cika da mamaki tare da cewa hakan ya nuna cewa Buhari na da koshin lafiyar da zai sake takara.

Sai dai mun duba mun hango cewa yan siyasa da dama kanyi abubuwan ban mamaki musamman a lokacin da zabuka suka gabato.

Sukan aikata abubuwan da jama’a basu taba tsammani daga gare su ba, don haka muka kawo maku wasu daga cikin hotunan abubuwan ban mamaki da sukan yi a wannan lokuta.

Ga sunan a kasa:

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)
Rotimi Ameachi yayinda yake yiwa wata mata kitso

KU KARANTA KUMA: Kungiyar matasan Arewa ta gargadi Miyetti Allah akan barazanar tsige Saraki daga kujerarsa

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)
Aisha Buhari yayinda take soya kosai

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)
Gwamna Rochas Okorocha na shayar da jariri abinci

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)
Gwamna Tanko Almakura kwance a katifar wasu yaran makarantar kwana

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)
Tsohon shugaban kasa Atiku Abubakar na in abinci cikin yara

Abubuwan ban mamaki da yan siyasa keyi kafin zabe (hotuna)
Shugaban jam'iyyar APC, Adams Oshiomhole tare da gwamnan jihar Edo, Obaseki suna cin dafaffen masara a hanya

Wannan kadan ne daga cikin abubuwan ban mamaki da yan siyasar kasar kan yi musamman a lokutan da aka ce zabe na gabatowa.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng