An kama soja da laifin fashi da makami da makaman gwamnati da ta bashi

An kama soja da laifin fashi da makami da makaman gwamnati da ta bashi

- An kama wani soja da laifin fashi da makami da kuma kungiyar asiri

- An damke shi ne yayin da yayi yunkurin kwace mashin

- Dan kungiyar asirin Black Axxe Confraternity ne

An kama soja da laifin fashi da makami da makaman gwamnati da ta bashi
An kama soja da laifin fashi da makami da makaman gwamnati da ta bashi

Yan sandan jihar Legas sun damke wani soja mai suna Daniel Okeke da laifin fashi da makami da kungiyar asiri.

An kama sojan bayan da yayi yunkurin kwace babur daga wani mutum a bangaren Agboju dake Legas.

DUBA WANNAN: Yadda aka yi zabe a Bauchi a yau

Bincike ya nuna cewa, wanda ake zargin Dan kungiyar Black Axxe Confraternity ne. An taba rage mishi matsayi a 2017 daga Kofur zuwa soja mai zaman kanshi bana an kama shi da laifin rashin kula da aiki.

Amma wanda ake zargin ya musa laifin da ake zargin shi dashi. Yace kawai ya samu rashin jituwa ne da mai babur din duk da yan sandan sun kama shi da pistol yana tsoratar da mai mashin din.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel