Shugaba Buhari ya yaba da ingancin kwarewar yan Najeriya a fannin ayyuka daban-daban a kasar Netherlands

Shugaba Buhari ya yaba da ingancin kwarewar yan Najeriya a fannin ayyuka daban-daban a kasar Netherlands

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nuna farin ciki da jin dadi kan yadda ya samu mutanen kasarsa Najeriya cike da kwarewa a kas Netherlands.

Shugaban kasar ya gana da mambobin kungiyar yan Najeriya a kasar waje, reshen kasar Netherlands, a ranar Litinin, 16 ga watan Yuli a ziyarar aiki da ya kai Hague, Netherlands.

Ya yiwa mutanen kasar nasa fatan akhairi a fannin ayyukansu daban-daban inda ya nuna jin dadinsa akan jajircewarsu.

Shugaba Buhari ya yaba da ingancin kwarewar yan Najeriya fannin ayyuka daban-daban a kasar Netherlands
Shugaba Buhari ya yaba da ingancin kwarewar yan Najeriya fannin ayyuka daban-daban a kasar Netherlands

Ya ce: “Na ji dadin irin kwararrun mutane da nake gani. Lallai kuna da tarin inganci. Ina taya ku murna kan nasarorin da kuka samu.”

KU KARANTA KUMA: Bana tsoron EFCC, ba zan gudu na bar Najeriya ba - Fayose

Ya yaba masu kan yadda suka daukaka martabar kasarsu Najeriya da kuma kasancewa tare da kasar a chan inda suke.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa kasar Netherland da misalin karfe 7:23 na yammacin Lahadi, 16 ga watan Yuli, don halartar taron Kotun Duniya, ICC, a birnin Hague na kasar, kamar yadda kamfanin dillancin labaru, NAN, ta ruwaito.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng