Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ta kai ziyara Nijar

Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ta kai ziyara Nijar

Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya (MDD), Amina Muhammad ta kai ziyara Jamhuriyar Nijar, inda a jiya taje Jihar Maradi don gabatar da ziyarar gani da ido

Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ta kai ziyara Nijar
Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ta kai ziyara Nijar

Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya (MDD), Amina Muhammad ta kai ziyara Jamhuriyar Nijar, inda a jiya taje Jihar Maradi don gabatar da ziyarar gani da ido, akan irin ayyukan da hukumomin Majalisar Dinkin Duniya ke yi a fannin ilimi, hakkokin yara, kiwon lafiya, da kuma kananan sana'o'i ga mata da kuma batun canjin yanayi a yankin.

DUBA WANNAN: 2019: Matasan Arewa sunce basu yadda shugaba Buhari ya zarce ba

A ranar Asabar din data gabata ne 7 ga watan Yulin wannan shekarar, Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniyar ta kai ziyara Jamhuriyar ta Nijar din.

A bayanin da Amina Muhammad din ta yi, ta bayyana cewa babban makasudin ziyarar ta ta shine domin karfafa samar da hakkokin mata a fanin ilimi, lafiya da kuma karfafa musu guiwa wurin shiga harkar siyasa domin tafiyar da al'amuran mulkin kasashen yankin yanda ya kamata.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel