Dandalin Kannywood: Rahama Sadau ta bayar da karin haske akan wanda za ta aura

Dandalin Kannywood: Rahama Sadau ta bayar da karin haske akan wanda za ta aura

Sanannar jarumar nan kuma shahararriya a masana'antar shirya fina-finan Hausa na Kannywood da kuma na fina-finan kudancin kasar nan watau Nollywood mai suna Rahama Sadau ta yi karin haske game da wanda ta ke so ta aure nan ba da dadewa ba.

Jarumar dai ta yi wannan bayanin ne yayin da take fira da wakilin majiyar mu a farkon wannan watan lokacin da ya tambaye ta ko ta taba yin aure a rayuwar ta.

Dandalin Kannywood: Rahama Sadau ta bayar da karin haske akan wanda za ta aura
Dandalin Kannywood: Rahama Sadau ta bayar da karin haske akan wanda za ta aura

KU KARANTA: Yadda wasu suka so kashe mani aure ina amarya - Mansura Isa

Yayin bada ansar ta ta dai jarumar dariya ta yi sannan ta bayyana cewa bata taba yin aure ba amma ta kusa in Allah ya so, kamar dai yadda ta ce.

Haka zalika a wakilin majiyar ta mu ya tambaye ta ko wanene masoyin nata kuma ko yana yin harkar fim ko ko ba ya yi sai jarumar ta yi togacciya ta bayyana cewa ba za ta iya sanar da sunan na sa ba a yanzu amma kuma sai ta tabbatar da cewa ba ya yin fim.

Da aka tambayi jarumar kuma ko meye alakar ta da Ali Nuhu musamman ma yadda jama'a ke danganta su da cewa su masoya ne, sai ta ce wannan maganar ba gaskiya bace domin ita Ali Nuhu yayana ne kuma ubangidana a wurin ta.

Daga karshe kuma sai jarumar ta bayyana cewa dukkan mace za ta so ta auri namiji irin Ali Nuhu din musamman ma saboda mutum ne nagari, mai tausayi da kyautatawa wanda kuma sune siffofin da duk wata mace ke nema.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel