Dubun wani mashahurin makashin maza daya addabi Funtua ta cika

Dubun wani mashahurin makashin maza daya addabi Funtua ta cika

Wani shahararren dan fashi a jihar Katsina mai suna Gojen-Mallam ya shiga hannun jami’an Yansanda a jihar Katsina, inji rahoton jaridar Daily Post.

Basiru Baurau mai sunan inkiya Gojen Mallam wanda ya kashe mutane uku a garin Funtua, an kama shi ne a ranar Laraba 28 ga watan Satumba, kamar yadda majiyar Legit.ng ta ruwaito Kaakakin rundunar Yansandan jihar yana fadi.

KU KARANTA: Ruwa ya ƙare ma ɗan kada: Budurwa ta saci wayar naira 170,000

DSP Gambo Isah yace; “Rundunar Yansandan jihar Katsina tana sanar da kama shahararren dan daban nan wanda aka dade ana nemansa Basiru Barau, inkiya Gojen Malam.

“Gojen Mallam ya kashe mutane uku, inda a ranar 30 ga watan Yuli 2014 ya kashe Aliyu Abubakar dake Hayin low-cost, haka zalika a ranar 4 ga watan Yuli ya kashe Abubakar Yusuf a gangaren gangariya. Sai kuma 7 ga watan Satumba 2017 ya kashe Samaila Idris.”

A yanzu dai ana cigaba da gudanar da bincike a kansa don kama sauran yan kungiyarsa, kuma za’a mika su gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: