Fada ya kacame tsakanin kasar Koriya ta Arewa da Amurka

Fada ya kacame tsakanin kasar Koriya ta Arewa da Amurka

- Rahotanni sun bayyana cewa Koriya ta Arewa ta gargadi Amurka da cewa a shirye take ta kakkabe jiragen ta domin tabbatar wa Amurka da karfinta na soji

- Gargadin Koriya ta Arewa na zuwa ne daidai lokacin da wasu jiragen ruwa na kasar Japan biyu ke wani atisaye da jiragen yakin Amurka a yankin yammacin Pacific

Shugaba Donald Trump ya bayar da umarnin wasu manyan jiragen kasar su keta gabar ruwan yankin na Koriya, a martaninta kan yunkurin Koriya ta Arewa na gwada makaman nukiliya da masu linzami.

Legit.ng ta samu labarin cewa ba a dai bayyana takamaiman wuraren da Amurkar ke hari ba a yankin, sai dai kalaman mataimakin shugaban Amurka na Asabar na cewa nan ba da jimawa ba ne jiragen za su isa.

Fada ya kacame tsakanin kasar Koriya ta Arewa da Amurka
Fada ya kacame tsakanin kasar Koriya ta Arewa da Amurka

KU KARANTA: Masarautar Kano ta shiga matsala

Koriya ta Arewa ta kuma kama wani dan kasar Amurka da ke kokarin ficewa daga kasar a jiya Lahadi, bayan kasancewar wasu Amirkawa biyu da ke tsare tun farko.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: