Kalli ‘ya’yan marigayi Yar’adua wadda dukkaninsu matan tsofaffin gwamnoni ne

Kalli ‘ya’yan marigayi Yar’adua wadda dukkaninsu matan tsofaffin gwamnoni ne

Kyawawan hotunan ‘ya’yan marigayi Yar’adua wanda dukkaninsu mataye ne ga tsofaffin gwamnoni a Najeriya.

Kalli ‘ya’yan marigayi Yar’adua wadda dukkaninsu matan tsofaffin gwamnoni ne
Marigayi Umaru Musa Yar'adua

Umaru Musa Yar’Adua ya kasance shugaban kasar Najeriya kafin rasuwar sa a shekarar 2010. Ya yi aiki a matsayin gwamnan jihar Katsina kafin ya hau kujerar shugabancin kasa. Yana auren Turai Umaru Yar’Adua sannan kuma sun haifi yara bakwai tare.

KU KARANTA KUMA: Anya wannan ne Buharin da aka sani kuwa- Inji wani Dan Majalisa

Uku daga cikin ‘ya’yan sa mata guda biyar na auren tsofaffin gwamnoni a yanzu. Hotunan matayen tsofaffin shugabannin ya yadu a yanar gizo sannan kuma Legit.ng ta gabatar maku da kyawawan matan.

Kalli ‘ya’yan marigayi Yar’adua wadda dukkaninsu matan tsofaffin gwamnoni ne
'ya'yan marigayi Umaru Musa Yar'adua

Dukkaninsu sun fito cikin shiga iri daya yayinda suka dauki hoto tare.

Maryam na auren tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema. Nafisat na auren tsohon gwamnan jihar Bauchi, Isa Yuguda yayinda Zainab ta kasance matar tsohon gwamnan jihar Kebbi, Usman Saidu Nasamu Dakingari.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Legit.ng ta hadu da wani matashi wanda ya iya zane sosai

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng