Amurka
Malamin addinin Musulunci, Dr. Ahmad Gumi ya ce Najeriya na bukatar taimakon kasashen waje kan tsaro, amma ba daga masu laifi, wariya ko masu tayar da zaune tsaye ba
Adamu Garba ya soki harin makamin Tomahawk da Amurka ta kai a Najeriya, yana mai cewa matakin ya raina martabar sojin kasar kuma yana barazana ga rayuwar farar hula.
Rahotannin da ke yawo cewa an kashe shahararren hatsabibin ‘yan bindiga, Bello Turji, a harin sama na kasar Amurka a jihar Sokoto ba gaskiya ba ne.
Ana zargin ‘yan ta’adda a yankin Arewa na fara guduwa daga maboyarsu bayan hare-haren sama da kasar Amurka ta kai a Sokoto da wasu sassan Najeriya.
Mai ba Shugaba Tinubu shawara kan yada labarai, Daniel Bwala ya bayyana hare-haren sama da Amurka ta kai wa ‘yan ta’adda a Sokoto a matsayin abin da ke da “ruɗani”.
Sanata Ali Ndume ya bukaci gwamnatin tarayya ta fadada hadin gwiwar sojojin Najeriya da Amurka zuwa Arewa maso Gabas saboda barazanar ISWAP da Boko Haram.
Dan majalisa a Amurka, Riley Moore, ya yi tsokaci kan harin da kasarsa ta kawo a Najeriya. Ya bayyana cewa harin ya hana kisan Kiristoci lokacin Kirsimeti
Jam’iyyar PDP a jihar Kwara ta caccaki gwamnatin AbdulRazaq kan yin shiru bayan fashewar bam a Offa, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin fargaba.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ya sauya ranar kai harin sojoji kan ’yan ISIS a Najeriya zuwa ranar bikin Kirsimeti domin wani dalili na musamman.
Amurka
Samu kari