Siyasar Najeriya
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya musanta jita-jutar da ake yaɗawa cewa ya gama shirin raba gari da jam'iyyar PDP kuma zai koma APC ko haɗakar ADC.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha ya musanta ikirarin cewa Shugab Tinubu ya maida Buhari shugaban ƙasa a zaben 2015, ya ce ba haka abin yake ba.
Sakataren jam’iyyar APC na kasa ya yi magana kan rade-radin cewa murabus din Abdullahi Ganduje zai jawo matsala a cikinta inda ya yabawa tasirin tsohon gwamnan.
Jam'iyyar ADC ta hadakar 'yan adawa ta bayyana cewa ba ta matsala d burin mayan jiga-jiganta na yin takarar shugaban kasa a babban zaben shekarar 2027.
Tsohon mataimakin shugaban APC na ƙasa kuma ɗaya daga cikin jagororin haɗaka, Salihu Lukman ya ce Obi ko Atiku, duk wanda ya samu nasara za a mara masa baya.
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore, ya yi magana kan shiga hadakar 'yan adawa. Ya ce da yawa daga cikinsu sun cutar da Najeriya.
Sanata mai wakiltar Benue ta Kudu a majalisar dattawa, Abba Moro, ya bayyana cewa zai ci gaba da zama daram a jam'iyyar PDP. Ya yi watsi da batun shiga hadaka.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Bababchir Lawal ya ce wasu manyan 'yan APC da gwamnoni na goyon bayan hadakar APC a boye domin kifar da Tinubu.
Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umar Radda ya bayyana cewa lokacin yaudarar ƴan Najeriya ya wuce, ya kamata haɗakar yan adawa su yi bayani kan tallafin fetur.
Siyasar Najeriya
Samu kari