Manyan Labarai A Yau
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa 'yan Najeriya sun kashe kudaden da suka kai N16tr wajen siyan janaretoci da man fetur domin samun lantarki a 2023.
Shugaban hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), Ola Olukoyede ya koka kan irin girman satar makudan kudaden da ake yi a kasar nan.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai hari kan manoma a karamar hukumar Jibia ta jihar Katsina. 'Yan bindigan sun hallaka mutum hudu har lahira a yayin harin.
Wani jami'i wanda ba a bayyana sunansa ba na hukumar yaki da masu yiwa tattaƙin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ya salwantar da ransa a birnin tarayya Abuja.
An samu asarar rayuka bayan aukuwar turmutsitsi a wurin wani taron addini a kasar Indiya. Da yawa daga cikin mutanen da suka rasa ransu mata ne da yara.
'Yan bindigan da suka sace mahaifiyar Dauda Adamu Kahutu wanda aka fi sani da Rarara sun bukaci a ba su N900m a matsayin kudin fansa kafin su sako ta.
Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta bayyana cewa jami'anta sun samu nasarar dakile harin da 'yan bindiga suka kai a Dutsinma. Sun ceto mutum 10 da aka sace.
Kungiyar gwamnonin yankin Kudu maso Gabas sun cimma matsaya kan batun shari'ar da ake yiwa shugaban kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu. Za su gana da Tinubu.
Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana cewa mai alfarma Sarkin Musulmi bai da ikon nada kowa a idon doka. Ta ce hakan ya sanya za ta yiwa doka gyara a jihar.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari