Manyan Labarai A Yau
Karamin ministan tsaro, Bello Matawalle, ya ba da tallafin tsabar kudi N20m ga mutanen da ambaliyar ruwa ta ritsa da su. Ya bukaci su rungumi kaddara.
Mataimakin gwamnan jihar Edo, Kwamared Philip Shaibu, ya shawarci Gwamna Godwin Obaseki na jihar da ya mutunta hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke.
Gwamnan jihar Plateau, Caleb Mutfwang ya dakatar da manyan jami'an gwamnatinsa mutum hudu. Gwamnan ya dakatar da kwamishinoni biyu da wasu jami'ai.
Kotun daukaka kara ta zartar da hukuncinta kan shari'ar tsige mataimakin gwamnan jihar Edo. Kotun daukaka karar ta tabbatar da Philip Shaibu a mukaminsa.
Rahotanni sun bayyana cewa Maria Branyas, wadda ta fi kowa a duniya ta mutu tana da shekaru 117. An ruwaito cewa an haifi Maria a 1907 kuma ta mutu a Spain.
Al'ummar mazabar Ondo ta Gabas/Ondo ta Yamma sun fara shirin yiwa dan majalisar da ke wakiltarsu a majalisar wakilai kiranye. Sun ce ya koma kasar waje.
Jam'iyyar NNPP ta sanar da kudaden da masu sha'awar tsayawa takara a zaben kananan hukumomin jihar Kano za su biya. NNPP ta sanya N600,000 a kujerar Ciyaman.
Gwamnatin jihar Sokoto ta amince da gina titin hanya wanda zai ba jami'an tsaro damar zuwa maboyar 'yan bindiga. Gwamnan ya ce ya shirya kare rayuka da dukiyoyi.
Tsohon shugaban kasa Janar Ibrahim Badamasi Babangida na daga cikin shugabannin da suka jagoranci kasar nan a mulkin soja. Ya cika shekara 83 a duniya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari