Manyan Labarai A Yau
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasara kan 'yan ta'addan Boko Haram a Borno. Sojojin sun hallaka miyagu tare da kwato kayayyaki masu yawa a hannunsu.
A yayin da aka bude gasar Big Brother Naija (BBNaija) zango na 10 a ranar Asabar, an samu mata uku da suka fito daga jihohin Arewa da suka shiga wannan gasa.
Tsohon mataimakin shugaban APC na ƙasa, Salihu Lukman ya bukaci shugabannin ADC sun shawo kan yunkurin jagororin haɗaka da ɗora wanda suke so a shugabanci.
Sabon shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya sha alwashin yin aiki tukuru don tabbatar da nasarar mai girma Bola Tinubu a 2027.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa an samu nasarori sosai a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu kan tsaro.
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya hango matsayar gwamnoni kan tazarcen shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027. Ya ce babu wanda zai yi adawa.
Gwamna Nwifuru ya dakatar da kwamishinoni 25 da wasu jami’ai 60 saboda rashin halartar taro, ya umarci su tafi hutu na wata guda ba tare da albashi ba.
Kansilolin Chanchaga sun dakatar da ciyaman dinsu, Aminu Ladan bisa zarge-zargen karkatar da dukiya, rashin bin doka da kin gabatar da bayanan kudade ga majalisa.
Jam'iyyar haɗaka watau ADC ta ce gwamnoni a shiyyar Kudu maso Gabashin Najeriya sun amince za su haɗe da ƴan adawa domin ceto ƙasar nan a zaɓen 2027.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari