Yaki da ta'addanci a Najeriya
A yayin da matsalar tsaro ke kara ci wa gwamnati tuwo a kwarya, Ministan tsaro, Mohammed Badaru ya yi kira ga kungiyar tarayyar Turai da ta tallafawa Nigeria.
Rundunar sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa wasu jami'anta guda hudu sun rasa rayukansu yayin da 'yan bindiga su ka kai musu hari a jihar Katsina
Dan majalisar Zurmi da Shinkafa ya bayyana cewa al'ummar kauyuka 50 a yankin Zurmi sun gudu sun bar gidajensu saboda yawan hare-haren ƴan bindiga a kwanan nan.
'Yan bindigar sun kai hari kauyen Benue inda suka bude wuta kan mai uwa da wabi, tare da kashe mutane 11 ciki har da wata mata mai dauke da juna biyu.
Rahotanni daga kananan hukumomin Maradun da Tsafe sun nuna cewa ƴan bindiga sun kashe manoma akalla 30 ciki har da malami a ƙauyuka biyu ranar Alhamis.
Wasu manya-manyan jami’an sojin kasar nan guda 29 sun yi ritaya bayan kamamala aiki da rundunar sojojin Najeriya. Sun kammala aiki ne ana tsaka da rashin tsaro.
Tsagerun ƴan bindiga sun kai hari kauyen Bilbis, sun kashe mazauna garin da dama da suka haɗa da maza, mata da kananan yara, sn yi masu jana'iza yau Jumu'a.
Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya ce tuni jami'an tsaro da mafarauta suka kaewaye daji da yankin jami'ar da ƴam bindiga suka kai hari jiya.
Rundunar yan sanda reshen jihar Katsina ta samu nasarar kuɓutar da mutane 13 da yan bindiga suka yi yunkurin yin garkuwa da su a kuyukan Malumfashi da Faskari.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari