Kotun Zabe: Hotunan Ban Dariya Yayin da Aka Gano Ganduje, Keyamo, Ozekhome Suna Likimo a Ranar Yanke Hukunci

Kotun Zabe: Hotunan Ban Dariya Yayin da Aka Gano Ganduje, Keyamo, Ozekhome Suna Likimo a Ranar Yanke Hukunci

  • A yanzu haka kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa na yanke hukunci kan kararrakin da aka shigar a kan nasarar Aswiaju Bola Tinubu
  • Kwamitin mutum biyar karkashin jagorancin Mai Shari'a Haruna Tsammani, ne za su yanke hukunci a kan zaben shugaban kasar da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu
  • Sai dai kuma, bidiyoyi da hotunan da ke nuna wasu manyan yan siyasa da lauyoyi suna sharbar bacci yayin zaman kotun ya ja hankali sosai

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jama'a sun yi cece-kuce yayin da wasu hotuna da bidiyoyi suka nuna wasu manyan yan Najeriya da lauyoyi suna sharban bacci a talbijin yayin da ake zaman kotun zaben shugaban kasa a ranar Laraba, 6 ga watan Satumba.

Manyan yan siyasar Najeriya na ta sharban bacci yayin da ake zaman kotu
Kotun Zabe: Hotunan Ban Dariya Yayin da Aka Gano Ganduje, Keyamo, Ozekhome Suna Likimo a Ranar Yanke Hukunci Hoto: Channels TV, @DeborahToluwase, @thecableng
Asali: Twitter

Daga cikin wadanda aka hango suna likimo awanni bayan shiga zaman kotun akwai tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban jam'iyyar All Progressives Congress na kasa (APC), Abdullahi Umar Ganduje; ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo.

Kara karanta wannan

Karin Bayani: Miyagun 'Yan Fashi Sun Kai Kazamin Hari Yankuna Uku a Babban Birnin Jihar PDP

Hakazalika, an hasko gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, Lauyoyi, da yan jaridu cikin masu sharar baccin, rahoton Daily Trust.

Jama'a sun martani kan haka a soshiyal midiya

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"RAHOTO NA MUSAMMAN: BACCI, WANDA BA A CIN BASHINSA...."Kimanin awanni hudu da fara zama, mutane da dama sun yi kokarin yakar bacci amma yan tsiraru ne suka yi nasara," rahoton The Cable.

Hadimin Sanwo-Olu ya yi martani yayin da Ganduje da sauransu suke bacci a kotun zabe

Da yake martani, Jubril A. Gawat @Mr_JAGs,hadimin gwamnan jihar Lagas, Babajide Sanwo-Olu ya wallafa hotunan wadanda ke bacci a kotun zaben sannan ya rubuta a shafinsa na X:

"IDANU a kan bangaren shari'a..#Hukuncin kotun zaben shugaban kasa."

Kotun zabe ta tabbatar da nasarar Abdulmumini Jibrin Kofa

A wani labarin kuma, mun ji cewa kotun sauraron kararrakin zaben yan majalisar tarayya da ke zama a Kano ta yanke hukunci cewa Muhammad Sa'id Kiru na jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ya gaza gabatar da shaidu da za su tabbatar da an tauye masa hakki a yayin zaben 2023.

Kotun zaben ta yi watsi da karar da ya shigar kan nasarar Abdulmumini Jibrin Kofa na jam'iyyar NNPP a ranar Laraba, 6 ga watan Satumba, Solacebace ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng