Katsina: Fusatattun Matasa Sun Cinnawa Fadar Basarake Wuta, An Yi Asara
- Matasa a garin Tsiga a jihar Katsina sun kone fadar dagacin garin bayan wani barawo ya nemi mafaka a can bayan ya daba wa mai babur wuka
- Jama’a sun bukaci a mika musu barawon amma aka hana, lamarin da ya tayar da hankali har ya kai ga kona fadar sarautar da ke Tsiga
- Wanda aka daba wa wuka yanzu yana cikin mawuyacin hali, yayin da lamarin ke kara tayar da kura a yankin karamar hukumar Bakori a Katsina
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Bakori, Katsina - An shiga tashin hankali a garin Tsiga da ke karamar hukumar Bakori a jihar Katsina da ke Arewacin Najeriya.
An ce wasu fusatattun matasa sun cinna wuta a fadar dagacin Tsiga da ke karamar hukumar bayan biyo wani barawo.

Source: Original
Katsina: Dalilin cinna wuta a fadar basarake

Kara karanta wannan
Yaran Turji na cin karensu ba babbaka, sun kora mazauna Sokoto, Zamfara daga gidajensu
Shafin Bakatsine da ke kawo rahoto kan tsaro shi ya tabbatar da haka a dandalin X a jiya Talata 13 ga watan Mayun 2025.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Majiyar ta ce matasan sun cinna wa fadar dagacin Tsiga wuta, bayan wani barawo da ya daba wa mai babur wuka ya tsere ya buya a can.
Jama’an gari sun bukaci a mika musu barawon, amma aka ki yarda wanda hakan ya jawo tashin hankali a tsakanin al’umma.
“Wanda aka daba wa wukar yana cikin mawuyacin hali yanzu."
- Cewar wani mazaunin yankin

Source: Facebook
Asarar da aka tafka a Katsina
Wasu rahotanni sun tattabar da cewa an samu asarar dukiyoyi sanadin haka wanda ya girgiza karamar hukumar Bakori.
Sanarwar ta ce:
"Fusatattun matasa sun kona fadar Dagacin Tsiga bayan wani barawo da ya daba wa wani direban babur wuka ya nemi mafaka a can.
"Jama’a sun bukaci a mika musu barawon, amma aka ki amincewa da hakan, lamarin da ya tayar da husuma a cikin garin.
"Wanda aka daba wa wukar yanzu yana cikin mawuyacin hali a asibiti, yana samun kulawa daga likitoci domin ceton rayuwarsa.
"Garin Tsiga na karkashin karamar hukumar Bakori a jihar Katsina da ke Arewacin Najeriya."
Karanta wasu labari da suka shafi Katsina:
- "Dogaran Sarki Sun Yi Ɓarna": Yadda Aka Yi Rikici a Wurin Bikin Auren Ɗiyar Gwamna Dikko
- 'Yan Bindiga Sun Zo Kwatar Abokinsu, Sojoji Sun Hallaka Hatsabibin Ɗan Ta'adda
- Dakarun Sojoji Sun Gwabza da 'Yan Ta'adda a Katsina, an Samu Asarar Rayuka
- Nazari: Ziyarar Tinubu a Jihar Katsina da Ra'ayin 'Yan Arewa gabanin Zaben 2027
An kona fadar babban Sarki a Edo
A baya, mun ba ku labarin cewa wasu fusatattun matasa sun kona fadar babban basaraken jihar Edo, Olojah na Ojah, Oba Okogbe Lawani.
Lamarin ya haifar da hatsaniya da tashin hankali a tsakanin mazauna garin Ojah da ke karamar hukumar Akoko-Edo a jihar Edo da ke Kudu maso Kudancin Najeriya.
An tabbatar da cewa rikicin ya samo asali ne a yayin birne wata mata da ake zargin ta mutu a cikin gidan tsafi a yankin wanda ya ɗaga hankulan mutane.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
