Zai Zama Abin Kunya Ga Gwamnonin Apc a Arewa Su Ci Dunduniyar Tinubu, Inji Gwamna Sule

Zai Zama Abin Kunya Ga Gwamnonin Apc a Arewa Su Ci Dunduniyar Tinubu, Inji Gwamna Sule

  • Gwamnan jihar Nasarawa ya bayyana kadan daga dalilan da suka sa APC ta ba dan takararta na shugaban kasa tikitin takara
  • Abdullahi Sule ya ce babu gwamnan APC a Arewa da ke adawa da tafiyar Asiwaju Bola Ahmad Tinubu a zaben 2023 na bana
  • Ya ce abin kunya ne ace wai akwai gwamnonin APC a Arewa na shirin cin dunduniyar dan takarar da suka aminta dashi

Najeriya - Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya ce, babban abin kunya ne ga gwamnonin APC a Arewacin Najeriya su ci dunduniyar dan takararsu na shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Sule ya bayyana hakan ne a lokacin da ya bayyana gidan talabijin na Channels.

Ya kara da cewa, gwamnonin APC a Arewacin Najeriya sun fito a baya don bayyanawa balo-balo cewa, suna son mulki ya koma Kudu, don haka suka marawa Tinubu baya a zaben fidda gwani.

Kara karanta wannan

'APC Ta Yi Babban Rashi a Arewacin Najeriya Wanda Ka Iya Shafar Su Tinubu a 2023'

Abin kunya ne a ce gwamnonin APC na Arewa za su ci amanar Tinubu
Zai Zama Abin Kunya Ga Gwamnonin Apc a Arewa Su Ci Dunduniyar Tinubu, Inji Gwamna Sule | Hoto: vanguardngr.com
Asali: Facebook

Ana yada jita-jita gwamnonin APC na shirin yaudarar Tinubu

Idan baku manta ba, ana yawan yada jita-jitan cewa, akwai lauje cikin nadi a APC, domin gwamnonin jam’iyyar a Arewa suna shirin marawa Atiku baya, Premium Times ta ruwaito.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Da yake magana, gwamna Sule ya ce:

“Na ji jita-jitan cewa wasu gwamnonin APC a Arewa basa yiwa Asiwaju Tinubu aiki. Zan yi matukar mamaki da kaduwa idan akwai wani gwamna.
“Idan za ka tuna, zai zama abin kunya ga gwamnonin APC a Arewa musamman a ce su juya mu ce ba sa son Asiwaju. Mutane ma za su mana dariya.
“Dalili kuwa shine lokacin da batun kujerar ya taso, gwamnonin APC a Arewa mun fito fili ba tare da boye-boye ba muka ce muna son kujerar nan ta bar Arewa ta koma Kudu.

Kara karanta wannan

Ya fasa kwai: Tinubu ya fadi makarkashin yin sabbin Naira da karancin mai a Najeriya

“Ta haka ne aka samar da Asiwaju. Don haka a ce wai wadannan gwamnonin da suka yi aiki tukuru kuma suka sa rayuwarsu a kan suna son mulkin karba-karba don yiwa kowa adalci a kasar a ce su ne kuma za su ci dunduniyar kai mulki Kudu (ba haka bane).
"Babu gwamnonin da ke hakan.”

A baya mun kawo muku rahoton da ke bayyana zarge-zargen wasu gwamnoni 11 da sanataoci da jiga-jigan siyasar da ke kokarin barin tsagin Tinubu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.